IBN TAIMIYYAH GWARZON NAMIJI. (Misbahu Abdullahi)
Shaikul islam Ahmad bn Abdulhalim ibn Taimiyyah Alharrany Addimashky ya rayu akarshen karni na bakwai zuwa farkon karni na takwas, ana kiran wannan lokaci da USURUL WUSDA. Shaihin musulunci ya taka mahimmiyar rawa aduniyar ta'alify, yai rubutu akan sufanci, yai akan kiristanci,yai akan shi'anci dsrns a janibin firak da sauran bangarori, malam ya gadarwa duniyar ilmi rubututtuka masu tarin yawa wanda bazai gusheba yana samun ladan wannan aikin Insha'allah har Allah yanade kasa, shaihi bai bar wata shubha ta ya'n bid'ah ko ya'n shi'ah ko wasunsu face saida yai kokarin byn kanta, har saida takai ya'n bid'ah da ya'n shi'ah na shakkar yatashi byni kansu suka shiga halin tsoro da firgici, ta kai sunansa aka ambata sai gabansu yafadi. Malam ya amsa sunan dodon ya'n bid'ah, har yazama babu mai adawa dashi sai dayan biyu: 1. Jahili:shikuma baisan wane shiba dole yai adawa dashi.
2.mai son xuciya: shikuma son xuciyarsa baxai barshi yabi gaskiyaba